Headlines
Loading...
Daliban Shari'a sun yi jarabawa a kan Ramos da Salah

Daliban Shari'a sun yi jarabawa a kan Ramos da Salah

Daliban Shari'a sun yi jarabawa a kan Ramos da Salah

Gumurzun da ya tursasa wa Mohamed Salah ficewa fili yana kuka a minti 30 a wasan karshe na gasar Zakarun Turai ya fito a jarabawar nazarin ilimin shari'a, kamar yadda aka ruwaito.
Hoton takardar jarabawar ta dalibai 'yan shekarar farko a jami'ar Damascus, ya mamaye shafukan Facebook na Syria.
An tambayi daliban cewar: "Sergio Ramos ya raunata Mohamed Salah a wasan karshe na lashe kofin Zakarun Turai.
"A bisa tsari, ba za a iya kama Ramos da laifin da ya aikata ba a dokar aikata laifuka ba, saboda wasu sharudda guda hudu da suka shafi rikici a wasanni. Fadi wadannan sharuddan."
Tambayar kamar an gamu ne da an dace musamman hamayyar wasan kwallon kafa da ke tsakanin daliban, yayin da wani shafin intanet na Enab Baladi da ke adawa ya bayyana malamin da ya shirya tambayar a matsayin "Dan Barcelona da ya sha kashi."
Real Madrid abokiyar hamayyar Barcelona dai ta lashe kofin gasar a Kiev bayan ta doke Liverpool 3-1.
Wani ya yi tsokaci a Facebook cewa: Duk wani magoyi bayan Barcelona zai yaga takardar jarabawar kuma ya fice bayan ya ji an ambaci sunan Ramos."
Wasu kuma sun yabi Farfesan da ya rubuta tambayar musamman ga daliban domin amfani da dokokin shari'a a wani abun da ya faru a zahiri.
Shafin Facebook na Jami'ar ya fitar da sanarwar da ke kare malamin. "Babu sarkakiya a Tambayar, dukkan godiya ga malamai baki daya."
Sanarwar ta kuma wallafa hoton tambayar, da kuma amsa, kuma wani dalibi ya amsa tambayar daidai kamar yadda shafin facebook na kafar Hawa TV ya wallafa
Amsar Sharudda guda hudu da aka tambayi daliban da aka wallafa su ne:
1 - An yi wasan ne a bisa doka.
2 - Dan wasan wanda ya ji rauni, ya amince ne ya buga wasan.
3 - Dan wasan da ya yi dalilin raunin, ya san dokoki da sharuddan wasan.
4 - Ga raunin da aka samu a lokacin wasan.

0 Comments: