Headlines
Loading...
An rushe Hukumar Kwallon Kafa ta Ghana

An rushe Hukumar Kwallon Kafa ta Ghana

An rushe Hukumar Kwallon Kafa ta Ghana

Gwamnatin Ghana ta rusa hukumar Kwallon Kafa ta kasar bayan da aka dauki bidiyon shugaban kungiyar yana karbar "na goro".

An dauki bidiyon Kwesi Nyantakyi yana karban dala 65,000 daga wani dan jarida mai binciken kwakwaf wanda yayi bad-da-kama, inda ya ce shi dan kasuwa ne mai sha'awar zuba jari a wasannin kwallon kafar kasar.

Sai dai kawo yanzu bai ce uffan game da tuhumar da ake masa.

Ministan wasanni na Ghana, Isaac Asiama ya ce an "rusa hukumar take-yanke", kamar yadda jaridar GhanaWeb ta ruwaito.

Manema labarai sun ce wannan tonon sililin aikin dan jaridar nan ne dan asalin kasar Ghana mai suna Anas Aremayaw Anas, wanda a sanadiyyar aikin nasa ya bankado ainihin badakalar da ake yi a fagen kwallon kafa a nahiyar Afirka.

A watan jiya aka mika wa hukumomin kasar fim din da ya hada mai suna "When Greed and Corruption Become the Norm", wato lokacin da hadama da rashawa suka zama jiki.

Ranar Laraba kuma aka nuna fim din a ko'ina cikin kasar da ma duniya.




0 Comments: