![An Ci Gaba Da Fasa Rumbunan Adana Kayan Abinci A Abuja](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEh67lLY8aRdNQ6FsfTocLf07iVgmeaJFB2Wts0Qg9KslpERKXJGlclDqnJHitx1jjWZk-EI8omX0timu2xzFNrDiuyjh4zSSTmTi82w9BWfo30efMgDsWY539xyo1isP-tHrFFuw96U9hwS/w700/Kayan-tallafi-scaled-e1603720524877.jpg)
Gungun matasa sun dora daga inda suka tsaya a ranar Lahadi, inda suka ci gaba da nemo rumbunan da aka boye kayan tallafin COVID-19 a Abuja.
Majiyarmu ta rawaito cewa mutane da dama ciki har da matasa sun bude rumbun adana abinci da ke yankin Gwagwalada a Birnin Barayya, Abuja.
Rahotanni sun bayyana cewa matasan sun ci gaba da kwasan kayan tallafi a rukunin masana’antu da ke Idu a Abuja.
A hangi mutane ciki har yara mata da maza suna dibar kayan tallafin da suka hada da shinkafa, taliya da sauran kayayyakin abinci.
A yanzu haka dai mutane na ci gaba da farautar rumbunan da aka boye kayan tallafin annobar COVID-19 a fadin Najeriya.
0 Comments: