Headlines
Loading...
An Ci Gaba Da Fasa Rumbunan Adana Kayan Abinci A Abuja

An Ci Gaba Da Fasa Rumbunan Adana Kayan Abinci A Abuja

An Ci Gaba Da Fasa Rumbunan Adana Kayan Abinci A Abuja

Gungun matasa sun dora daga inda suka tsaya a ranar Lahadi, inda suka ci gaba da nemo rumbunan da aka boye kayan tallafin COVID-19 a Abuja.


Majiyarmu ta rawaito cewa mutane da dama ciki har da matasa sun bude rumbun adana abinci da ke yankin Gwagwalada a Birnin Barayya, Abuja.


Rahotanni sun bayyana cewa matasan sun ci gaba da kwasan kayan tallafi a rukunin masana’antu da ke Idu a Abuja.


A hangi mutane ciki har yara mata da maza suna dibar kayan tallafin da suka hada da shinkafa, taliya da sauran kayayyakin abinci.


A yanzu haka dai mutane na ci gaba da farautar rumbunan da aka boye kayan tallafin annobar COVID-19 a fadin Najeriya.

0 Comments: