Headlines
Loading...
Yan Siyasa ne suka kitsa labarin EFCC za ta bincike ni – Wamakko

Yan Siyasa ne suka kitsa labarin EFCC za ta bincike ni – Wamakko

Shugaban Zauren Sanatocin Arewacin Najeriya, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, Sanata mai wakiltar Sakkwato ta Tsakiya a majalisar dattijai ta Najeriya, ya bayyana cewar wasu ‘yan siyasa da ke adawa da shi ne suka kitsa labarin wai hukumar EFCC za ta bincike shi kan badakalar biliyan 15 da aka batar a lokacin mulkinsa, har an ga wasu biliyan daya da rabi a asusun ajiyarsa na banki. 

Ya kara da cewar “Wallahi ban taba mallakar naira biliyan daya ba a rayuwata ta duniya”. Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai a makon da ya gabata a gidansa da ke Unguwar Gawon Nama a Sakkwato ya ce ‘ni ba mutum ne mai kudi ba, hakazalika b ana aje kudi’.

Wannan bayanin ya biyo baya ne a lokacin da Sanata Wamakko yake karin haske ga labarin karya da wasu jaridun Najeriya suka wallafa akan cewar hukumar EFCC tana tuhumarsa da satar kudi da shi da tsohon Gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.
A cikin labarin da wadannan jaridu suka wallafa, sun bayyana cewa wannan zargi ya biyo baya ne ta hannun wasu mutane da suka rubuta koke zuwa ga Hukumar EFCC, inda suke neman a binciki Sanata Wamakko wanda suke hasashen ya kwashi kudin al’umma da suka cimma biliyan 15 a lokacin da yake a matsayin Gwamnan Jahar Sokoto.

Sanatan ya kara da cewar “dukkan abin da wadannan mutane suka bayyana a cikin kokensu da suka rubuta zuwa ga hukumar EFCC karya ne, magana ce maras tushe, kuma kiren karya ne da yake tattare da zarge-zarge na karya daga mutane masu yada zancen karya da jita-jita a cikin al’umma, ba magana ce ta hukumar ba ta wasu mutane ce dole sai sun karya Wamakko sun manta da Allah dai da ya halicce shi ke iya karya shi, maganar an ga biliyan 1 da rabi a asusuna ba wani hankali da zai yarda da ita duk masu hankali sun gane wannan labari ne aka shirya don cin zarafina.” 

Aliyu Wamakko ya ce, dukkan wadannan abubuwa na zarge zarge suna daga cikin shirye-shirye na makiyansa da kuma ‘yan siyasa da suka sha faduwa zabe a lokacin gwagwarmayar siyasa da shi wanda kuma har yau suka zama abun kyama ga al’ummar jahar, haka ma su ne mutane da suke neman ganin cewa Sanata Wamakko ya daina numfashi a duniya. Sun sha rubutawa EFCC takardu har an taba rubutawa a gidan wani dan siyasa wai jami’a mallakar jiha da na gina da gidajen Mana da Kalambaina ba a yi su ba, aka ga ya yi karya. “Ni ban fadi ba na kuskure ba, in na aiwatar da lamari a bincike ni cikin adalci da gaskiya.” 

 “A mulki na yi iyakar kokarina da sadaukarwa kan amanar da aka damka min na samar da manyan makarantun gaba da sakandare biyar da gidaje sama da dubu biyar har da gidajen Alkalai, kilomita 1,000 na titin kwalta da samar da sana’o’i da matasa dubu 500, bayan samar da kananan asibitocin mazabu da motocin daukar marasa lafiya, a lokacin ina gwamna ba na yawo, bani yin sati daya bana cikin jihata, na ziyarci Amurka da Landan sau daya kuma shi ma gayyata ce na samu,” a cewar Sanata. 

“Wannan bincike da ake magana ya dace ya kasance bisa ka’ida da gaskiya, kuma hakika ni na tabbatar cewa ban saci kudin kowa ba. A matsayina gwamnan Sakkwato daga shekarar 2007 zuwa 2015, na gudanar da jagoranci da kwatanta gaskiya a cikinsa, da kula da amanar da talakawan Sakkwato suka damka min ba tare da yin coge ba. 

“Na kalubalanci mutane da suke yada wannan karya a jaridu da cewar, su wallafa hakikanin gaskiyar takardun bayanai na asusun ajiya na na bankuna wanda yake nuna hakan, don a gane ba sharri da karya ce ba.

0 Comments: