Headlines
Loading...
Yadda na zama Mataimakin Shugaban kasa –Osinbajo

Yadda na zama Mataimakin Shugaban kasa –Osinbajo

Mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo ya bayyana cewa Shugaba Muhammadu Buhari ne ya zabe shi mataimakinsa bayan ya yi shawara da Jam’iyyar APC inda suka yi takara tare kuma suka ci zabe a shekarar 2015.

Osinbajo wanda ya bayyana haka lokacin da yake amsa tambayoyin da daliban makarantar Life Camp suka yi masa yayin bikin ranar littafi ta duniya a makon da muke ciki.

“Bayan da shugaban kasa ya gana da jam’iyarmu sai ya yanke shawarar nada ni wanda zai zama mataimakinsa inda muka tsaya takara tare muka tsaya zabe kuma muka yi nasara a zaben shekarar 2015,” in ji shi.

Ya bayyana cewa kafin lamarin yana koyar da aikin lauya ne a jami’ar Awolowo da ke Jihar Legas. Da yake amsa tambaya kan samar da kayayyakin more rayuwa a Najeriya, sai ya ce samar da kayan more rayuwa hakki ne na gwamnati tare da hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu.

Ya kara da cewa gwamnati ita take da alhakin samar da hanyoyi da asibitoci da makarantu da sauran kayan more rayuwa. Ya bayyana cewa gwamnati na karawa kamfanoni kwarin gwiwa don su ma su tallafa wajen samar da kayan more rayuwa ga al’ummar kasa baki daya.

Da aka tambeye shi ko yana da sha’awar zama shugaban kasa sai ya ce “Ni yanzu matsayina na mataimakin shugaban kasa ne”. Daga nan sai ya bayyana cewa lamarin mulki abu ne mai mutukar wahalar gaske saboda nauyin da ke tattare da shi.

0 Comments: