Headlines
Loading...
Abin da ya sa za mu lashe zabukan kananan hukumomin Kaduna – Shugaban APC

Abin da ya sa za mu lashe zabukan kananan hukumomin Kaduna – Shugaban APC

Shugaban Jam’iyyar APC a karamar Hukumar Jama’a da ke Jihar Kaduna, Alhaji Ibrahim Aliyu Koli ya ce a shirye jam’iyyarsu take don tunkarar zaben shugabannin kananan hukumomin Jihar Kaduna da ke tafe don lashe kananan hukumomin jihar gaba daya.

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyin Aminiya a ofishin jam’iyyar da ke Kafanchan. Ibrahim Koli, ya kara da bayyana cewa aikace-aikacen da gwamnan jihar yake shimfidawa a ko ina a fadin jihar Kaduna da suka hada da gyaran kananan asibitoci da makarantun firamare da shimfida hanyoyi da inganta harkokin tafiyar da mulki sun isa zama shaida kan dalilin lashe zabukan da ke tafe.

“Duk surutan da ‘yan adawa za su yi sai dai su yi na son zuciya amma dai kowa ya san idan rana ta fito babu wani tafin hannu da zai iya kare ta daga haskakawa,” in ji shi.

Da ya waiwaya kan matsalolin cikin gida na APC, ganin yadda wata ‘yar takara a karamar hukumar Jama’a ta buga fostocinta tana yadawa a matsayin halastacciyar ‘yar takarar shugabancin jam’iyyar domin raba hankulan jama’a, alhali akwai Kwamred Cecelia Musa wacce ita ce halastacciyar ‘yar takarar jam’iyyar a karamar hukumar, inda ya ce masu yin haka a kowace karamar hukuma suna batawa kan su lokaci ne domin hukumar zabe ta jiha ta san wanene ba wanene ba.

0 Comments: