Headlines
Loading...
Najeriya za ta ba Ecowas dala miliyan 20 na yaƙi da ta’addanci

Najeriya za ta ba Ecowas dala miliyan 20 na yaƙi da ta’addanci

Najeriya za ta ba Ecowas dala miliyan 20 na yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Najeriya ta ce ta ware dala miliyan 20 zuwa ga ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka Ecowas domin yaƙi da ta’addanci a yankin.


Ministan harakokin wajen Najeriya Geoffrey Onyeama ne ya shaida wa taron shugabannin ƙasashen karo na 58 da aka gudanar a ranar Asabar.

Ministan ya ce tuni Najeriya ta bayar da umurnin fitar da kuɗaɗen zuwa ga asusun Ecowas.


Ya kuma ce gwamnati ta ware dala miliyan 80 domin yaƙi da ƴan ta’adda a arewa maso gabashin Najeriya da kuma ƴan fashin daji a arewa maso yammacin ƙasar.


Matsalar tsaro musamman ta’addancin Boko Haram da IS a yankin ƙasashen na yammacin Afirka ne ya mamaye taron shugabannin.


Shugaban Nijar Mahamadou Issoufou ya faɗa wa taron shugabannin na Ecowas cewa ta’addanci ne babbar barazanar da yankin sahel ke fuskanta.

0 Comments: