Headlines
Loading...
Ƴan bindiga sun sace mutum 15 a jirgin ruwan Turkiya a Najeriya

Ƴan bindiga sun sace mutum 15 a jirgin ruwan Turkiya a Najeriya

Ƴan bindiga sun sace mutum 15 a jirgin ruwan Turkiya a Najeriya

Wasu ƴan bindiga a tekun Najeriya sun kashe wani matuƙin jirgin ruwa tare da yin awon gaba da wasu 15 da ke cikin jirgin ruwa mai dakon kaya na Turkiya, kamar yadda kamfanin dillacin labarai Anadolu na Turkiya ya ruwaito a ranar Lahadi.


Kamfanin dillacin labaran ya ce wanda aka kashe ɗan asalin ƙasar Azerbaijan ne.


Kafar yaɗa labarai ta NTV a Turkiya ta yi magana da ɗaya daga cikin matuƙa jirgin ruwan da ke ciki wanda ya ce wasu da dama sun ji rauni.

Jirgin mai suna Mozart na kan hanyarsa ce daga Legas a Najeriya zuwa birnin Cape Town na Afirka ta Kudu wanda ya taso a ranar Asabar.


An bayyana cewa yanzu ya kamo hanya yana kusa da Gabon.


Yan fashin teku a Najeriya sun yi kaurin suna wajen sace matuka jirgin ruwa inda ko a 2019 an taba sace matuka jirgin Turkiya kafin aka sake su a watan Agustan 2019.

0 Comments: