Headlines
Loading...
Dubban mutane na son a hukunta Sergio Ramos kan Mo Salah

Dubban mutane na son a hukunta Sergio Ramos kan Mo Salah

'Yan sandan Merseyside sun ce suna sane da sakonnin barazanar kisa da ake aike wa golan Liverpool Loris Karius bayan wasan karshe na gasar zakarun Turai.

An rinka turawa dan kwallon na kasar Jamus, mai shekara 24, da iyalansa sakonnin barazana bayan kuskure biyu da ya yi wanda ya taimaka wa Real Madrid ta doke su da ci 3-1 a wasan na ranar Asabar.

Karius ya barke da kuka bayan an tashi daga wasan sannan kuma ya nemi afuwar magoya baya.
"Muna daukar irin wadannan sakonnin da ake wallafa wa a shafukan zada zumunta da muhimmanci. Za mu yi binciken kan dukkan laifukan da aka aikata," a cewar 'yan sanda.

"Jami'ai na sane da sakonnin barazana da aka tura ta shafukan sada zumunta.
"Muna tunatar da masu amfani da wadannan shafuka cewa za a binciki duk wata al'amari da halayya mai kama da wannan."

Dan wasan ne ya bai wa Karim Benzema kwallon farko da ya ci cikin sauki.

Daga bisani Karius ya kasa tare kwallon da Gareth Bale ya buga daga nesa wacce ta bai wa Madrid damar saka kwallo ta uku da kuma lashe kofin.

0 Comments: