Headlines
Loading...
An bukaci Pantami ya ɓullo da tsarin toshe layi idan an sace saboda NIN

An bukaci Pantami ya ɓullo da tsarin toshe layi idan an sace saboda NIN

An bukaci Pantami ya ɓullo da tsarin toshe layi idan an sace saboda NIN

Yayin da gwamnatin Najeriya ta ɓullo da sabon tilastawa ƴan ƙasar haɗa layukansu na salula da kuma lambobinsu na katin shedar ɗan ƙasa, wani ɗan ƙasar ya bayyana damuwa kan makomar layin mutum idan ɓarayi sun sace.


Gambo Muhammad a sahafinsa na Twitter @gambomuhammad6 ya ba ministan sadarwar ƙasar Sheikh Pantami shawara ya ɓullo da tsarin yadda mutum zai toshe layinsa idan har an sace layin.


Ya buƙaci a samar da wasu lambobi da mutum zai iya aikawa ya toshe layinsa idan an sace.


Ministan kuma ya amsa cewa ya karɓi shawarar tare da gode masa, sai dai bai bayyana ko shawarar da aka ba shi ba za ta samu ga ƴan Najeriya.

0 Comments: