Headlines
Loading...
Abubuwa Da Suka Janyo Guguwar Fasa Dakunan Abinci A Najeriya

Abubuwa Da Suka Janyo Guguwar Fasa Dakunan Abinci A Najeriya

Manyan Abubuwa Da Suka Janyo Guguwar Fasa Dakunan Kayan Abinci A Najeriya

Jim kadan bayan kawo ƙarshen zanga-zangar nuna adawa da zaluncin da ake zargin jami'an 'yan sanda na yi a Najeriya, wani batu da ya sake kunno kai shi ne yadda wasu matasa ke kutsa wa ɗakunan ajiyar abinci na gwamnati suna wawashe abubuwan da aka jibge a ciki.


Yayin da gwamnatocin jihohin da lamarin ya faru ke cewa sun adana kayayyakin ne, jama'ar gari na cewa boye su aka yi, dalilin kenan da ya sanya suka fusata domin karbar abin da suke ganin hakkinsu ne a matsayinsu na ;yan kasar.


Rahotanni sun ambato yadda irin wannan al'amari ya faru a jihohi da dama, kama daga kan na kudanci da zanga-zangar End SARS da kuma wadanda ba'a yi ba, dalilin kenan da yasa hukumomi daukar matakai daban-daban domin shawo kan lamarin.


Ana danganta abubuwan da ke faruwa da tunzurar da jama'a suka yi sakamakon zanga-zangar da aka kwashe tsawon makwanni ana yi a wasu jihohi.


Wasu daga cikin irin kayayyakin da aka jibge a irin waɗannan gidaje sun haɗar da nau'ukan abinci iri-iri da aka tanada don raba wa mutanen da annobar korona ta fi shafa, wasu na gwamnatin tarayya ne da ta raba wa jihohi, wasu kuwa jihohin ne suka tara ta hanyar karɓar gudummawa daga masu hannu da shuni da masu sha'awar taimaka wa jama'a.


Abin da yawancin matasan da ke irin wannan ƙundumbala ta wawashe kayan da aka tanada a gidajen ajiyar abinci na gwamnati ke cewa shi ne me yasa za a boye abinci alhalin na jama'a ne?


Ga shi kuma an yi nisa a cikin wannan annoba da aka tanadi kayan dominta, sannan an ƙi raba wa mutane har yanzu?


Ita dai gwamnati a nata ɓangaren na kallon hakan a matsayin laifi, sai dai wasu na ganin cewa al'amarin na ƙara fito da halin ƙunci da takura da jama'a ke ciki, lamarin da a yanzu ya fara muni har ta kai sun fara ɗaukar wannan mataki domin su ci su rayu.


Fargabar da ake da ita a yanzu ita ce idan ba a ɗauki mataki ba, watakila masu irin wannan ɗabi'a za su koma kan kayan jama'a da zarar sun gama da na gwamnati.


Ga dai wasu dalilai huɗu da masu sharhi ke ganin sun taka rawa wajen guguwar da ta kawo fasa ɗakunan kayan abinci a Najeriyar.

Talauci


Talauci ya ƙaru a Najeriya kamar yadda rahotanni daban-daban suka nunar, ita kanta gwamnatin kasar ta amince da haka, ta sha neman afuwar jama'a tare da yin alƙawarin cewa abubuwa za su daidaita nan da ɗan wani lokaci.

Karuwar farashin kayan masarufi da kara farashin litar man fetur ta janyo sauye sauye da dama, wasu na ganin cewa wannan hali da ake ciki ya taimaka matuka gaya wajen faruwar irin wannan al'amari

Kwamared Kabiru Sa'idu Dakata wani ɗan gwagwarmaya ne, kana mai sharhi kan al'amuran da suka shafi al'umma, ya ce ba dai-dai ba ne gwamnati ta ɓoye abincin da aka raba wa jama'a musamman lokacin da aka shiga kulle, amma a ajiye su alhalin ga halin da mutane ke ciki na buƙata, kuma an san jama'a ba za su kasa sanin cewa akwai su ba.

''Gwamnatin tarayya ta sanar a hukumance, cewa ta bada wannan tallafi, wasu ma kungiyoyin kasashen duniya ne suka bayar, jama'a sun samu labari, amma sai aka yi shiru ba'a raba su ba''in ji Comrade Kabiru Dakata, dan gwagwarmaya mai sharhi kan al'amuran yau da kullum.

Ya ce matsawar mutane na ganin cewa gwamnati ta ɓoye tare da hana su haƙƙinsu alhalin cin yau da na gobe na gagararsu babu abin da zai hana su daukar wannan mataki, duk da cewa hakan ba dai-dai ba ne.

Rashin yarda tsakanin al'umma da gwamnati

Wasu rahotanni sun nuna cewa kayan abincin sun jima a ajiye, wasu jihohin ma sun ce suna fargabar cewa mutanen da suka kwashe suna iya gamuwa da cututtuka domin har lokacin amfaninsu ya wuce.


Irin wannan na iya kawo rashin yarda tsakanin jama'a da kuma hukumomi, domin zargin da mutum zai iya shi a nan shi ne me yasa ba a raba su ba har aka bari suka lalace?


''Ɓoye kayan abinci da wasu jihohi suka yi, ya nuna cewa ba mahaifina ne ke da laifi a taɓarɓarewar al'amura ba'' in ji Zahra Buhari, ɗiyar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.


Wasu mutane a shafukan sada zumunta na kallon kalaman a matsayin ƙoƙarin wanke kai daga zargin da ka iya biyo baya, sai dai wasu na ganin cewa rijiya ce ta bayar da ruwa guga ya hana.


Ɓata gari


Hukumomi na cewa matasan da ke wawushe kayan ɓata gari ne, sai dai wasu rahotanni sun nuna cewa yawancinsu jama'ar gari ne da ke rayuwa a inda rumbunan ajiyar suke.

Hotunan yadda lamarin ya faru a wasu wurare sun nuna yawancin mutanen masu iyali ne, da kuma yara ƙanana da ma dattawa, baya ga hoton wani mai lalurar naƙasa da aka dasawa ƙafa da shi ma ya yi ta yawo a shafukan sada zumunta.

Ba abin mamaki ba ne idan gwamnati na danganta su da ɓata gari, duba da cewa lamarin na zuwa ne jim kadan bayan kammala lalata gine-ginen gwamnati da kuma kwashe kayan jama'a a wasu jihohi da zanga-zangar End SARS ta rikiɗe ta zama tashin hankali a cikinsu.

Sannan ba abin mamaki ba ne idan zanga-zangar ta taimaka wajen fusata jama'a domin ƙwatar abin da suke ganin cewa hakkinsu ne duk da cewa a baya ba a ga hakan ta faru ba

Taɓarbarewar tsaro


Wasu masu sharhi na cewa matsalar rashin tsaron da ake fama da shi a wasu sassan ƙasar da ya jefa mutane cikin halin ha'ula'i na raba su bda muhallansu da mayar da su ƴan gudun hijira, ya taka rawa wajen sa wasu su zama cikin masu rububin abincin.

A hannu guda kuma ga duk wanda ya ji irin abubuwan da ke faruwa a baya-bayan na abin da zai zo masa shi ne ina jami'an tsaron da aka ajiye domin gadin irin wadannan wurare?

Bayanai sun nuna cewa ba shakka a kan ajiye jami'an tsaro domin kula da waɗannan kayayyakin abinci amma a wasu wurare da dama da irin hakan ta faru yawan mutanen da ke wawashe kayan abincin ya kai intaha har ya sa jami'an tsaron suka dinga roƙon jama'a da su yi a hankali ban da turereniya, kamar yadda aka gani a wasu bidiyon.

Ga kuma fargabar kada garin hana mutane ɗibar kayayyakin a samu asarar rai, irin abin da ya faru a baya na zanga-zanga ya sake maimaita kansa.

To sai dai duk da haka, jami'an tsaron na cewa suna daukar matakan sake tsaurara tsaro a gidajen domin tabbatar da kare kayayyakin gwamnati

Jihohi da dama sun lashi takobin gano mutanen da suka wawashe kayayyakin tare da daukar mataki a kansu.

0 Comments: